in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kenya ta yi gargadi akan bazuwar sakonnin hare haren al-shabaab
2016-02-03 10:16:45 cri
Hukumomin kasar Kenya sun yi gargadi akan baza sakonnin akan hare hare na al-shabaab da takardun sakonnin dake bayyana wanda ke tafe daga bangaren kungiyar dake Somaliya a gundumar Mandera dake arewa maso gabashin kasar.

Kwamishinan Gundumar Manhera, Frederick Shisia yace wadansu kungiyoyi masu zaman kan su tuni suka fara janye wassu ma'aikatan su domin tsoron wannan hari da kungiyar masu tsatsauran ra'ayin addini ke yi dalilin sakonnin nuna kiyayya da ake ta bazawa ta kafofin sada zumunta.

Yace kungiyoyi masu zaman kansu suna janye ma'aikata daga kananan gundumomin Banisa, Takaba da Mandera ta gabas.

Mr. Shisia a hirar shi da manema labarai a gundumar Manderan yayi bayanin cewa mayakan al-shabaab wadanda a watan jiya suka hallaka sojojin kasar Kenya da dama a lokacin harin a kudancin Somaliya, suna cigaba da canza salo, yana mai lura da cewa sakonni na da nufin saka tsoro ne a zukatan jama'a da kuma korar kungiyoyi masu zaman kansu.

Ya tabbatar da cewar an lura'yan kungiyar sun canza salon a dabarun kai harin su. Don haka salon jami'an tsaron shi ma ya canza domin a tunkare su gaba da gaba.

Kwamishinan gundumar har ila yau yace jami'an tsaro dake kula da muhimman wurare da suka hada da Fino,Jillo, Dabacity, Lafey da kuma Arabiya sun riga sun mamaye ko ina tare da dawo da tsaron su.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China