in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon MDD yace an fara tattaunawar cikin gida na Syria a hukumance bayan ganawa da 'yan adawa
2016-02-02 10:15:31 cri
Manzon Musamman na MDD a kasar Syriya Staffan de Mistura a ranar litinin din nan ya sanar da cewar an fara tattaunawar Geneva na cikin gidan Syria ya a hukumance bayan da aka gana da tawagar 'yan adawa a karon farko.

De Mistura ya shaida ma manema labarai bayan ganawa da 'yan adawan a yammacin wannan rana cewar batun jin kai da 'yan adawan suka kawo a lokacin ganawar shi ma wani murya ne na jama'ar kasar kuma dole a saurari muryar a lokacin tattaunawar.

Yace ba kawai za'a yi tattaunawa a Geneva bane har ma za'a samar da wani abu da al'ummar Syrian zasu gani su kuma taba. Yana mai bayanin cewa rikicin kasar Syrian ya riga dade har shekaru shida a cikin shekara na 6 al'ummar kasar ne sun wahala kwarai don haka dole a samu wani sabon abu a cikin tattaunawar.

Yace zai gana da wakilan gwamnatin kasar Syrian a talatan nan sannan tawagar zasu yi tattaunawa mai zurfi akan batutuwan da yafi jawo hankalin kowa a baya bayan nan musamman muhimmin batu na dakatar da bude wuta.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China