in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban kasar Sin ya halarci taron Davos na 2016
2016-01-22 10:27:30 cri
Mataimakin shugaban kasar Sin Li Yuanchao ya halarci taron tattaunawar tattalin arziki na shekara-shekara na duniya na 2016 da aka yi a birnin Davos na kasar Switzerland, inda ya yi jawabin fatan alheri a gun taron musamman da aka shirya game da tattalin arzikin kasar Sin da taron kolin kungiyar G20 na shekarar 2016.

Mr. Li ya ce, yanzu, ana shiga wani muhimmin mataki na kara kuzari game da raya tattalin arzikin duniya, kuma tattalin arzikin Sin ya bunkasa yadda ya kamata. A shekarar 2015, saurin bunkasuwar tattalin arzikin Sin ya ci gaba da kasancewa a sahon gaba a duniya, kuma ya zama ginshikin raya tattalin arzikin duniya. Kasar Sin na da kwarewa wajen raya tattalin arziki cikin sauri, kuma za ta bi manufar kirkiro da sabbin abubuwa da daidaita saurin bunkasuwa kuma ba tare da gurbata muhalli ba, da cin gajiyar fasahohin da aka samu, wannan zai taimaka wajen raya tattalin arziki cikin sauri. Kasar Sin kuma za ta ci gaba da bin manufar samar da zaman lafiya da samun bunkasuwa, da hadin gwiwa, da samun moriyar juna tare, don fuskantar kalubale tare da ragowar kasashen duniya.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China