in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Masar sun kaddamar da baje kolin raya al'adu don kara fahimtar juna
2016-01-15 10:53:27 cri
Ma'aikatar raya al'adu ta kasar Masar da ofishin jakadancin kasar Sin a Masar sun kaddamar da shirin raya al'adu tsakanin kasashen biyu na shekarar 2016, domin murnar tunawa da cika shekaru 60 da kafuwar huldar diplomasiyya tsakanin Sin da Masar.

Ministan raya al'adun kasar Masar Helmy al-Namnam, ya shedawa kamafanin dillancin labaran kasar Sin Xinhua cewar, bikin raya al'adun na shekara-shekara zai kara dankon zumunta dake tsakanin kasashen biyu.

Wannan sanarwa ta zo ne a yayin taron manema labaru a birnin Alkahira na kasar .

An sanya shekarar 2016 a matsayin shekarar mai armashi ga dangantakar dake tsakanin kasashen biyu ne tun a yayin wata ganawa tsakanin shugaba Xi Jinping na kasar Sin da takwaransa Abdel-Fattah al-Sisi na kasar Masar a watan Disambar shekarar 2014 a birnin Beijing.

Masar ita ce kasa ta farko a kasashen Larabawa a nahiyar Afrika da ta fara amincewa da kasar Sin.

A nasa bangaren minista mai kula da ofishin jakadancin kasar Sin a Masar Qi Qianjin, ya ce dangantakar dake tsakanin Sin da Masar tana kara samun bunkasuwa ne a kullum.

Qi ya kara da cewar, Masar ita ce kasar da ta fara kafa cibiyar raya al'adun Sinawa a kasarta, sannan ita ce kasar da ta hada Sin da sauran kasashen Larabawa.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China