in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya: Cutar zazzabin Lassa ta bulla a Abuja
2016-01-14 19:39:17 cri
Rahotanni daga ma'aikatar lafiyar tarayyar Najeriya, na cewa yanzu haka an samu bullar cutar zazzabin Lassa a birnin Abuja fadar mulkin kasar. Ya zuwa yanzu dai cutar ta bazu zuwa jahohin kasar 10, inda a birnin na Abuja mutum guda ya rasa ransa a Alhamis din nan, bayan garzayawa da shi asibiti, kuma likitoci suka tabbatar da cewa cutar ta Lassa ce ta hallaka shi.

Da yake karin haske game da lamarin, ministan ma'aikar lafiyar kasar Isaac Adewole, ya ce ya zuwa yanzu, mutane 42 ne suka rasa rayukan su sakamakon kamuwa da cutar. Sai dai duk da hakan ministan lafiyar ya ja hankalin mazauna birnin na Abuja da kada su razana, su kuma dauki matakan lura, tare da kai rahoton cutar da zarar sun ga alamun ta.

Mahukuntan Najeriyar dai na cewa suna da kwarewa, da kuma ikon dakatar da yaduwar cutar ta Lassa, kuma akwai kyakkyawan hasahen samun maganin ga masu dauke da ita, muddin dai sun garzaya asibiti a kan lokaci.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China