in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD ta sabunta takunkumi a kan ta'addancin da ta kakaba ma Afghanistan
2015-12-22 10:30:28 cri
Kwamitin sulhun MDD a ranar litinin din nan ta kara wa'adin takunkumin data kakaba ma kungiyoyin ta'addanci a kasar Afghanistan tare da bayyana matukar damuwan ta a kan yanayin tsaro musamman sakamakon tashin hankalin da ake fuskanta yanzu da ayyukan ta'addanci da kungiyoyin al-qai'da, Taliban da kuma alaka mai karfi tsakanin ta'addanci da hare hare da kuma safarar miyagun kwayoyi.

Kwamitin ya bayyana matukar damuwa game da karuwan kungoyoyin ta'addanci a yanzu da kuma nan gaba na kungiya mai tsattsauran ra'ayi da ake kira ISIL dake da alaka da Afghanistan.

Kwamitin ta kara wa'adin takunkumin wanda ya hada da daskarar da asusun ajiyar su, hana su tafiye tafiye,da kuma takunkumin makamai a kan daidaikun mutane da kungiyoyi.

Sai dai kuma , kwamitin ta lura da yadda yanayin tsaro da ake ciki a Afghanistan ya sassauta kuma wassu mambobin Taliban sun yi sulhu da gwamnatin kasar tare da goyon bayan a sulhunta tashin hankalin da ake cigaba da fuskanta a kasar ta hanyar lumana.

A don haka, kwamitin ta bayyana aniyar ta na cire takunkumin a kan wadanda suka yi sulhu.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China