in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Rwanda ya gode ma al'ummar kasar bisa ga zaben raba gardama da suka yi
2015-12-22 10:16:46 cri
Shugaban kasar Rwanda Paul Kagame a ranar litinin din nan ya gode ma al'ummar kasar sakamakon zaben raba gardama a kan gyaran fuska a kundin tsarin mulkin kasar wanda zai ba shi daman sake neman takara bayan karshen wa'adin shi a shekara ta 2017, duk da cewar bai furta wannan bukata ba tukuna.

A cikin jawabin da ya yi ma al'ummar kasar a Kigali babban birnin kasar, Shugaba Kagame ya yi watsi da kudurin kasashen yammaci na gurgunta sakamakon zaben raba gardamar a kan kundin tsarin mulkin kasar. Sakamakon zaben na ranar jumma'a ya nuna cewar kashi 98% sun jefa amincewar su.

Amurka ta bayyana rashin jin dadin ta cewar an shirya zaben raba gardamar a cikin kankanin lokacin don yin gyara a kundin tsarin mulkin kasar da kuma cire tsawon wa'adin shugaban kasar a ciki.

A cikin sanarwar da fadar white house ta fitar ranar asabar, ta ce bayan yaba ma al'ummar kasar Rwanda na aiwatar da 'yancin su lami lafiya , Amurka ba ta ji dadin yadda zaben bai ba da wadataccen lokaci da dama ga muhawaran siyasa ba a kan alfanu ko rashin alfanun abin da ake niyyar yi.

Tawagar kungiyar tarayyar Turai a Rwandan ita ma ta bayyana damuwar ta cewa mako daya da aka shirya aiwatar da zaben raba gardamar kasar ba ta yi bayani sosai akan sauyin da za'a yi a cikin kundin tsarin mulkin ba balle ta samar da lokacin isashe da dama na yin muhawara.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China