in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-Moon ya nuna damuwa game da harin roka kan Israila
2015-12-22 09:51:00 cri
Babban magatakardar MDD Ban Ki-moon ya bayyana damuwar sa, game da harin roka da dakarun kasar Lebanon suka kaddamar a wasu yankunan kudancin Isra'ila, yana mai cewa hakan ya sabawa yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

A ranar Lahadin karshen mako ne aka harba wasu rokoki daga wajen birnin Tyre na Lebanon zuwa Isra'ila, lamarin da ya sanya Isra'ilan maida martani kan garuruwan Qolaile da al-Mansouri na Lebanon.

Wata sanarwa da kakakin Mr. Ban ya fitar, ta ce tawagar MDD mai aikin wanzar da zaman lafiya dake Lebanon wato UNIFIL,na gudanar da bincike da hadin gwiwar mahukuntan rundunonin sojojin kasar Lebanonda na Isra'ila domin gano bakin zaran.

Mr. Ban ya kara da cewa UNIFIL na fatan dukkanin sassan da wannan tashin hankali ya shafa zasu kai zuciya nesa, su kuma kaucewa daukar matakan da ka iya rura wutar rikici.

Yarjejeniya mai lamba 1701 da kasashen biyu suka amincewa a shekakar 2006, ta kai ga cimma nasarar dakatar da dauki ba dadi tsakanin Hezbollah da dakarun Israila, bayan shafe kwanaki 33 suna musayar wuta.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China