in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zai yi wuya a tabbatar da cewa Iran ta taba kera makaman nukiliya cikin rahoton IAEA
2015-11-27 11:15:30 cri
Shugaban hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA Yukiya Amano ya bayyana cewa, a cikin rahoton da hukumar IAEA za ta fidda, zai yi wuya a iya amsa cewa, ko Iran ta taba nazarin kera makaman nukiliya.

Mr.Yukiya Amano ya fada wa manema labaru cewa, game da zargin da aka yi wa Iran cewa, wai tana gudanar da shirin kera makamin nukiliya cikin siri, wannan batu ne mai sarkakiya, don haka, hukumar IAEA ba ta da tabbas a kai. Mambobin hukumar za su tsaida kuduri bisa wannan rahoto, ciki har da ko za a kawo karshen batun nukiliya na kasar Iran ko a'a a yayin taron majalisar zartaswar hukumar. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China