in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mali ta cafke mutane 2 da ake zargi da hannu cikin harin ta'addanci da aka kai a otel
2015-11-27 10:12:21 cri
Hukumar tsaron kasar Mali ta fidda wata sanarwa a jiya Alhamis, wadda ke cewa, sojojin kasar sun cafke wasu mutane 2 da aka tuhuma da hannun cikin harin da aka kai a otel din Radisson BLU dake birnin Bamako, fadar mulkin kasar.

Sanarwar ta ce, sakamakon hadin gwiwar hukumar lekan asiri da wasu mutanen da abun ya shafa, rundunar sojin kasar ta samu nasarar cafke mutanen 2. Bayan gudanar da bincike ne kuma aka gano cewa wadannan mutane sun fito ne daga wata unguwa da ke wajen birnin Bamako. Yanzu haka dai ana ci gaba da binciken wadannan mutane 2.

Wani jami'in bincike da ya nemi a boye sunan sa, ya shaidawa manema labaru cewa, an samu wata wayar salula a wurin da aka kai harin, wadda ta taimaka ainun wajen cafke wadannan mutane.

Idan dai ba a manta ba, a ranar 20 ga watan nan na Nuwamba ne aka kai harin ta'addanci kan otel din Radisson BLU dake birnin Bamako, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 20, tare da harbe mahara 2 a wurin. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China