in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwararrun kasar Rasha sun binciki yanayin filayen jiragen sama na kasar Masar
2015-11-09 13:52:14 cri
Kasar Rasha ta tura kwararru zuwa kasar Masar, domin bincike kan yanayin filayen jiragen sama na kasar, yayin da kimanin mutane dubu 15 daga cikin 'yan kasar Rasha dubu 80 da aka dakatar a kasar ta Masar, sakamakon abkuwar faduwar jirgin sama a kwanakin baya, suka riga suka koma gida.

Mataimakin firaministan kasar Rasha Dmitry Medvedev ya umurci gwamnatin kasar sa da ta tsara wani shiri, domin taimakawa kamfannonin yawon shakatawa da suka ci karo da hasara a sakamakon daina zirga-zirgar jiragen sama zuwa kasar Masar. Har ila yau, kawo yanzu ba a kai ga samun cikakken dalilin faduwar jirgin saman kasar ba tukuna.

A game da labarin da hukumomin leken asiri na kasashen Amurka da na Birtaniya suka bayar, cewa wai jirgin saman ya fadi ne a sakamakon fashewar boma-boman da aka sanya a cikin kayayyakin fasinjan jirgin sama, kwamitin bincike ya bayyana cewa, bai samu shaidu ko kadan da za su tabbatar da hakan ba.

Domin tabbatar da tsaro, kasashen Birtaniya da Faransa da Jamus da Turkiya da kuma Saudiyya sun sanar da dakatar da saukar jiragen saman su a birnin Sharmel Sheikh na kasar Masar. Yayin da ita kuma Rasha ta soke sufurin dukkan jiragen saman ta zuwa kasar Masar tun daga ranar 6 ga wata. (Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China