in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manyan jami'an diplomasiyyar Sin sun gana da shugaban taron M.D.D. karo na 70
2015-10-29 09:46:46 cri
Mamban majalissar gudanarwar Sin Yang Jiechi, da ministan harkokin wajen kasar Wang Yi sun gana da shugaban taron M.D.D. karo na 70 Mogens Lykketoft a jiya Laraba 28 ga wata.

A yayin ganawar tasu, Yang Jiechi ya ce, an samu sakamako mai gamsarwa a yayin jerin tarurrukan da aka shirya don tunawa da kafuwar M.D.D., matakin da zai haifar da muhimmin tasiri game da makomar M.D.D., da kyautata alakar kasa da kasa.

Taron M.D.D. karo na 70 na da hakkin gudanar da ayyuka don cimma burin da aka saka a gaba yayin tarurrukan kolin M.D.D. da aka yi a baya, kuma kasar Sin za ta ci gaba da nuna goyon baya game da taron M.D.D.

Yayin da Mista Wang Yi ke ganawa da Lykketoft, ya ce, Sin ta nuna cikakken goyon baya ga M.D.D., kuma za ta bi tunanin da shugaban Xi Jinping ya gabatar a yayin taron koli na baya, don ganin M.D.D. ta samu ci gaba, tare da bude sabon shafin inganta hadin gwiwa tsakanin sassan biyu.

A nasa bangare kuma, Lykketoft ya jinjinawa babbar gudummawar da Sin ta bayar a yayin tarurrukan koli na M.D.D., yana mai yabawa muhimmiyar rawar da Sin ke takawa game da batutuwan M.D.D. Ya kuma yi fatan inganta hadin gwiwa da kasar Sin a cikin wa'adinsa. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China