in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jakadan Sin a Amurka ya jaddada matsayin Sin game da kutsa kai cikin yankin teku na tsibiran Nansha da jiragen ruwan yakin Amurka suka yi
2015-10-28 10:41:06 cri
Yayin da jakadan Sin a Amurka Cui Tiankai ke zantawa da manema labaru na CNN na Amurka a jiya Talata 27 ga wata, ya sake jaddada matsayin da Sin ta dauka kan batun kutsa kai cikin yankin tekun tsibiran Nansha na kasar da jiragen ruwan yaki na Amurka suka yi.

Jakadan Cui ya ce, kutsa kai cikin ruwan kasar Sin da jiragen ruwan yaki na Amurka suka yi ya zama babbar barazana, kuma kasar Sin da jama'ar kasar dake fatan samar da zaman lafiya a wannan yanki sun dora muhimmanci sosai game da lamarin.

Ya kara da cewa, matsayin da Amurka ke tsayawa a kai game da batun tekun Nanhai tamkar almara ce. A bangare guda ma, ta bukaci sauran bangarorin da kada a rura wuta ta hanyar yin shisshigin soji a yanki, sannan a dayan bangare, ta tura jiragen ruwan yaki zuwa yankin.

Jakadan Cui ya sake nanata cewa, kasar Sin na da ikon mulkin kai a tekun kudancin ta tun asali. Har ila yau in ji Mista Cui,Kasar Sin za ta dauki kwararran matakai don tabbatar da cin gashin kanta da cikakken ikonta, don samar da zaman lafiya da karko a yankin.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China