in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-Moon ya yi kira ga bangarorin daban-daban na Kongo(Brazzaville) da su warware rikici tsakaninsu cikin ruwan sanyi
2015-10-22 13:53:59 cri
Babban magatakardan M.D.D. Ban Ki-Moon ya ba da wata sanarwa ta kakakinsa a jiya laraba, inda ya dora muhimmanci sosai kan halin kunci da ake ciki tsakanin gwamnati da bangaren adawa na kasar Kongo(Brazzaville).

A game da gyaran fuska ga tsarin mulkin kasar kuma Ban Ki-Moon, ya yi kira ga bangarorin daban-daban na kasar da su warware batun cikin lumana sannan har ila yau a cikin sanarwar, Magatakardar na MDD ya yi kira ga bangarorin daban-daban da su yin shawarwari kafin jefa kuri'ar raba gardama.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, game da soke ka'idojin dake shafar wa'adin tazarcen shugaban kasar a cikin sabon tsarin mulkin kasar, bangaren adawa na kasar Kongo(Brazzaville)da magoya bayansa sun yi zanga-zanga a birnin Brazzaville kwanan baya, don nuna adawa akan hakan.abinda ya kawo tashe-tashen hankali tare da yin sanadiyyar mutuwar mutane da jikkatar wasu da dama.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China