in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta fara aiwatar da shirin fitar da jerin sana'o'i da ayyukan da za a haramta zuba jari a kansu a kasar a shekarar 2018
2015-10-20 14:33:38 cri
Jiya Litinin ne shafin Intanet na gwamnatin kasar Sin ya fitar da wata takarda game da shirin da yak e na fitar da jerin sana'o'i da ayyukan da za a haramta zuba jari a cikin su a kasar, inda aka bayyana cewa, daga watan Disambar bana zuwa karshen shekarar 2017, za a fara gwajin wannan shirin a wasu yankunan kasar, sannan ya zuwa shekarar 2018 za a fara aiwatar da wannan shirin a fadin kasar Sin baki daya.

Majalisar gudanarwar kasar Sin ce ta bayar da wannan takarda, inda ta bayyana karara cewar, za ta fitar da jerin sunayen sana'o'i da fannoni da ayyukan da za a haramta zuba jari a kansu a kasar Sin, inda ta bukaci gwamnatoci a matakai daban daban na kasar Sin da su kwararran dauki matakan aiwatar da shirin. Ban da wadannan sana'o'i da fannoni da ayyukan da gwamnatin ta haramta, za a iya gudanar da ayyukan kasuwanci kamar yadda doka ta tsara. Sannan kuma an kasa jerin sunaye gida 2, wato jerin sunayen sana'o'i da za a haramta dukkan 'yan kasuwa na gida da na waje su zuba jari a cikin su a kasar Sin, gami da jerin sunayen sana'o'i da za'a haramtawa 'yan kasuwa na ketare zuba jari a cikin su.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China