in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Afrika da dama sun gudanar da atisayen soji
2015-10-20 10:57:26 cri
Daga ranar 19 ga watan Oktoba zuwa ranar 7 ga watan Nuwamba, kasashe da dama na kungiyar AU na gudanar da atisayen soji a cibiyar horar da sojojin kasa dake jihar Northern Cape dake kasar Afrika ta Kudu, inda 'yan sanda da sojoji sama da 5400 da suka fito daga kasashe mambobin kungiyar AU da dama suka halarci atisayen.

Makasudin atisayen soji na wannan karo shi ne warware matsalolin tsaro na Afrika bisa karfin kanta, da tantance kwarewar rundunar ASF ta Afrika, don cimma burin gudanar da aikin soji daga duk fannoni kafin watan Disambar shekarar bana.

Rundunar ASF za ta kunshi sojoji 25000 da suka fito daga kasashen yammacin Afrika, da na arewacin Afrika, da na gabashin Afrika da kuma kudancin nahiyar, wadanda za su zama ginshikin sojojin tabbatar da zaman lafiya da karko a Afrika. Nauyin da ke wuyansu shi ne nacewa kan horaswa don mayar da martani kan shirin ko-ta-kwana. Haka zakila idan M.D.D. ko kungiyar AU suka bukace ta, za su iya gabatar da roko, don amfani da su.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China