in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dole a hukunta masu laifi da harbo jirgin saman Malaysia MH17
2015-10-15 09:26:20 cri
Firaministan Malaysia Najib Tun Razak ya bayyana a ranar 14 ga wata a birnin Kuala Lumpur cewa, bayan fitar da rahoton karshe game da hadarin jirgin sama mai lamba MH17, an tabbatar da cewa, an harba shi ne daga yankin gabashin kasar Ukraine da rokar da Rasha ta kera, Malaysia da bangarori daban-daban da batun ya shafa za su dauki kwararan matakai, don tabbatar da hukunta masu laifi da wadanda suke da hannu cikin wannan ta'asa.

A ranar Talata da ta gabata ne, masu bincike suka fidda sakamakon bincike a kasar Holland, inda suka yi imani cewa, roka samfurin Buk ce ta yi sanadiyyar hadarin jirgin saman. Game da wannan, a ranar laraban nan 14 ga wata, Rasha ta nuna tsayayyiyar adawa game da wannan. Wani jami'in ma'aikatar zirga-zirgar jiragen saman Rasha ya ce, rahoton da Holland ta bayar, ya wuce gona da iri.

A ranar 17 ga watan Yulin shekarar bara, jirgin sama mai samfuri MH17 da ya taso daga Amsterdam a kan hanyarsa ta zuwa birnin Kuala Lumpur na kasar Malaysia, ya fadi a yankin gabashin kasar Ukraine da ke kusa da kan iyaka da kasar Rasha, abin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 298 dake cikin .(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China