in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Turkiya: Adadin mutanen da suka mutu a cikin tagwayen fashawa ya karu zuwa 95
2015-10-11 13:27:00 cri
Adadin mutanen da suka mutu a cikin tagwayen fashewar boma bomai a ranar Asabar a Ankara, babban birnin Turkiya, ya karu zuwa 95, a cewar wata sanarwa ta fadar faramininsta Ahmet Davutoglu. Fashewar boma boman sun shafi wata tashar jirgin kasa, a yayin da kungiyoyin kwadago, kungiyoyin fararen hula da jam'iyyar tabbatar da demokaradiyyar ta al'ummar Turkiya, dake goyon bayan Kurdawa, suke gudanar da wani taron gangami, a cewar kamfanin dillancin labarai Dogan mai zaman kansa. Taron gangamin ya shafi nuna adawa da yakin da ake yi tsakanin gwamnatin Turkiya da mayakan 'yan aware na Kurdawa a kudu maso gabashin kasar Turkiya.

Ya zuwa yanzu babu wata kungiyar da ta dauki alhakin kai wannan harin. A cewar wasu da lamarin ya faru gaban idonsu, lamarin fashewar boma-bomai ya faru har sau biyu a filin dake gaban tashar jirgin kasa.

Shugaban Turkiya, Recep Tayid Erdogan ya yi alla wadai da wannan hari, wanda a cewarsa yake neman kawo baraka ga hadin kan 'yan kasa.

Turkiya na shirin gudanar da zabuka a ranar 1 ga watan Nuwamba, a cikin wani yanayi na tashin hankali da rikici tsakanin jam'iyyun siyasa, wadanda suka kasa kafa wata gwamnatin hadaka a yayin zabukan watan Yuni.

Sakatare janar na MDD, Ban Ki-moon ya yi allawadai a ranar Asabar da wannan harin ta'addanci na Ankara, tare da aike da ta'aziyarsa ga iyalan mamatan.

Haka kuma, a cikin wannan sanarwa ta kakakinsa, mista Ban ya nuna fatan ganin an gurfanar da masu hannu kan wannan hari gaban kuliya cikin gaggawa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China