in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rikici a tsakanin sojojin Guinea ya haddasa mutuwar mutum guda
2015-10-10 13:48:03 cri
Sojoji magoyon bayan shugaban kasar Guinea Alpha Condé da na 'yan adawa sun yi arangama a daren ranar alhamis 8 ga wata, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum guda, tare da jikkatar wasu 20.

Ministan kula da harkoki cikin gida na Guinea Mamoudou Cisse ya ba da wata sanarwa ta wani gidan rediyon kasar, inda ya yi Allah wadai da tashe-tashen hankali dake kawo illa game da zaman rayuwar jama'a da zaman lafiyar al'umma kafin babban zaben kasar.

A cikin sanarwar, an ce, ko magoyon bayan gwamnatin ko na 'yan adawa, ya kamata sojoji su bi akidar samar da zaman lafiya sannan su kai zuciya nesa. Sai dai ba a ambaci wurin da arangamar ta faru ba tsakanin 'yan adawan da sojojin.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China