in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta mika ta'aziyar ta ga iyalan wadanda suka rasu a turmutsitsin Saudia
2015-09-25 19:39:42 cri
A yau jumma'a Kasar Sin ta bayyana matukar juyayin ta game da hasarar rayukan da aka yi da kuma wadanda suka jikkata a turmutsitsin da ya faru a Mina lokacin aikin hajji na kasar Saudia.

Kamar yadda kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin Hong Lei ya bayyana ma manema labarai a nan birnin Beijing, yace Sin tana mika ta'aziyar ta tare da juyayi ga iyalan wadanda suka rasu ko suka jikkata.

Mahukuntar kasar Saudiya sun tabbatar da cewar akalla mutane 717 ne suka rasu. Wannan ne karo na biyu da irin haka ya faru cikin wata daya. A farkon watan maniyyata 111 suka rasu sanadiyar faduwar karfen daukan kaya wanda ya fado daga ginin masallacin Harami da ake fadadawa a birnin Makka.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China