Hukumar tsaro da kare rayukan jama'a ta Saudi Arebiya ne ta sanar da karuwar adadin a shafin ta na twitter.
Wadanda iftila'in ya rutsa da su, sun fito ne daga kasashen duniya dabam dabam.
Lamarin dai ya afku ne a daidai lokacin da mahajjatan ke ta tururuwar jifar shaidan, wanda daya ne daga cikin rukunonin aikin hajjin.(Ahmed)