in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta fidda tsari na samar da daidaito tsakanin jinsi da raya harkokin mata a kasar
2015-09-22 11:27:09 cri
Ofishin yada labaru na majalisar gudanarwar Sin ya fidda takardar bayani game da samar da daidaito tsakanin bambancin jinsi da raya harkokin mata, wanda ke kunshe da babban ci gaba da Sin ta samu a wannan fanni.

A yayin taron manema labaru da aka shirya a yau, kakakin ofishin yada labaru na majalisar gudanarwar Sin Hu Kaihong ya bayyana cewar, takardar bayanin ta kunshi alkaluma da abubuwan da ke faruwa a kasar, kana an nuna matakan da Sin ta dauka wajen samar da daidaito tsakanin bambancin jinsi da raya harkokin mata, da ma ci gaban da aka samu a kasar.

Mr. Hu ya ce, wannan ya kasance takardar bayani na uku da gwamnatin Sin ta fidda wajen raya harkokin mata, kuma an fidda takardu da harsunan Sinanci da Turanci da Faransanci da Rashanci da Jamusanci da Larabci da kuma harsunan Spaniya da Japan.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China