in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu hare-haren bama-bamai sun halaka mutane a kalla 9 a Najeriya
2015-09-21 20:50:02 cri
Rahotanni daga Najeriya na cewa, a kalla mutane 9 ne suka halaka kana wasu 45 suka jikkata, a wasu sabbin hare-hare da ake zaton mayakan Boko Haram ne suka kai a a jihar Borno da ke arewa maso gabashin kasar.

Wani ganau mai suna Bulama yusuf ya bayyana cewa, wani dan kunar bakin wake ne ya tayar da bam na farko a cikin wani masallaci a unguwar Ajilari a birnin Maiduguri,fadar mulkin jihar Borno mai fada da tashin hankali, harin da ya halaka mutane 9 tare da jikkata wasu mutane 15.

Ya ce, mituna biyar bayan harin farko sai kuma wasu bama-baman suka tashi a unguwar Gomari inda nan ma mutane sama da 30 suka jikkata. Bayanai na cewa, motocin 'yan sanda na hukumar bayar da agaji sun kai wadanda suka jikkata zuwa asibitocin da ke kusa.

Kakakin rundunar sojojin Najeriya Kanar Sani Usman Kukasheka ya tabbatarwa kamfanin dillancin labarai na Xinhua aukuwar lamarin, sai dai bai yi wani karin haske game da harin ba. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China