in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a cimma nasarori masu armashi a ziyarar da shugaban kasar Sin zai kai Amurka
2015-09-17 21:38:44 cri
A yau Alhamis ne, ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin ta kira taron manema labarai dangane da ziyarar da shugaban kasar Sin zai kai kasar Amurka tare da halartar jerin tarurukan MDD a mako mai zuwa, inda jami'in ma'aikatar ya ce, ziyarar ba kawai za ta kai ga kara amincewa da juna da inganta huldar da ke tsakanin Sin da Amurka kawai ba, har ma za ta kawo nasarori masu armashi ta fannoni daban daban.

Mai ba da taimako ga ministan harkokin waje na kasar Sin Mr. Zheng Zeguang ya ce, ta wannan ziyara, ba kawai bangarorin biyu za su iya zurfafa hadin gwiwarsu ta fannonin ciniki da aikin soja da makamashi da kiyaye muhalli da zirga-zirgar sararin sama ba, har ma za su kai ga kara daidaitawa da juna a fannonin bunkasuwar tattalin arzikin duniya da sauyin yanayi da kiyaye zaman lafiya, tare kuma da cimma daidaito a kan batutuwan da suka shafi yankin Asiya da tekun Pasifik da batun nukiliyar kasar Iran da na zirin Koriya da ma batun Afghanistan da sauran harkokin shiyya shiyya. (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China