in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaiministan kasar Guinea-Bissau ya yi murabus
2015-09-10 11:16:06 cri
Sabon Firaiministan kasar Guinea-Bissau Baciro Dja ya sanar da yin murabus daga mukaminsa bayan da ya gana da shugaban kasar Jose Mario Vaz a jiya Laraba. Dja ya bayyana cewa, ba zai iya ci gaba da zama Firaiministan kasar ba a karkashin yanayin siyasar da kasar ke ciki.

Gabannin daukar wannan mataki, kotun kolin kasar ta yanke hukunci cewar, nada Baciro Dja a matsayin Firaiministan kasar da Jose Mario Vaz ya yi ya saba tsarin mulkin kasar.

A bisa tsarin mulkin kasar ta Guinea-Bissau, shugaban jam'iyyar da ta lashe zaben 'yan majalisu shi ne ya dace ya zama Firaiministan kasar. A watan Mayun shekarar bara ne dai, Jose Mario Vaz ya lashe babban zaben kasar bayan da ya yi takarar a jam'iyyar PAIGC kuma ita ce jam'iyya mafi girma a kasar, kuma bayan nasarar tasa ne ya nada shugaban jam'iyyar Domingos Simoes Pereira ya zama Firaiministan kasar. A ranar 12 ga watan Agusta na wannan shekarar, Jose Mario Vaz ya sanar da wargaza gwamnatin dake karkashin jagorancin Domingos Simoes Pereira, a sakamakon rashin jituwa a tsakanin su. Ka zalika a ranar 20 ga watan Augasta ne, Jose Mario Vaz ya nada tsohon ministan harkokin taron ministoci da majalisu Baciro Dja ya zama sabon firaministan kasar, ba tare da la'akari da ra'ayin adawa da jam'iyyar PAIGC ta nuna.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China