in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afirka ta kudu za ta karbi bakuncin taron FOCAC
2015-09-05 12:45:31 cri
Shugaba Jacob Zuma na Afirka ta Kudu ya bayyana aniyar kasarsa ta karbar bakuncin kaso na biyu, na babban taron tattaunawa game da hadin gwiwar Sin da kasashen nahiyar Afirka da aka yi wa lakabi da FOCAC na shekarun 2012 zuwa 2018. Taron da ake sa ran gudanarsa a watan Disambar karshen wannan shekara.

Shugaba Zuma wanda ya bayyana hakan a ranar Jumma'a gabanin komawarsa gida, bayan halartar taron cika shekaru 70 da cimma nasarar yakin kin harin Japanawa da ya gudana a nan birnin Beijing, ya kara da cewa kasarsa za ta karbi bakuncin wannan taro mai muhimmanci a matsayinta na daya daga shugabannin taron na FOCAC, wanda ake fatan zai samu halartar shugabannin nahiyar Afirka, da shugabannin hukumomin kasa da kasa da na shiyya-shiyya.

Ya ce Sin da nahiyar Afirka na da alaka mai fadi, kuma yanzu lokaci ya yi da sassan biyu za su kara inganta gajiyar da suke ci daga juna, ta fuskar bunkasa masana'antu, da samar da ababen more rayuwa.

Wannan dai taro da Afirka ta Kudu za ta karbi bakunci shi ne na irin sa na farko da zai gudana a nahiyar Afirka. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China