in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mahukuntan kasar Sin sun bukaci a kara kokarin ba da jinya ga wadanda fashewar Tianjin ta shafa
2015-08-13 09:21:15 cri

Shugaba Xi Jinping na kasar Sin da Firaminista Li Keqiang sun yi kira da a dauki dukkan matakan da suka dace na ganin an ceto rayukan wadanda suka jikkata da kuma rage duk wata barna da za ta iya biyo baya sakamakon fashewar da ta faru a birnin Tianjin da ke arewacin kasar Sin

Bugu da kari, shugaba Xi ya ba da umurnin daukar matakan gano wadanda suka bace tare da kashe wutar da ta tashi sanadiyar fashewar.

A nasa bangare firaminista Li ya lashi takwabin ganin an gudanar da cikakken bincike don gano musabbabin hadarin da ya faru.

Yanzu haka dai majalisar gudanarwar kasar ta Sin ta aike da wata tawagar bincike karkashin jagorancin ministan kula da harkokin tsaron jama'a Guo Shengkun don jagorantar aikin ceton gaggawa a wurin da hadarin ya faru

Masu aikin ceto dai sun bayyana cewa, mutane 17 ne suka mutu kana sama da 400 suka jikkata sanadiyar fashewar da ta faru a ranar Laraba da dare a wani dakin ajiye kayayyaki a birnin na Tianjin mai tashar jiragen ruwa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China