in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ofishin jakadancin kasar Sin ya shirya taron tsaron abinci a Sudan
2015-08-11 21:37:56 cri
Ofishin jakadancin kasar Sin dake kasar Sudan, ya shirya wani taron yini biyu, domin tattauna muhimman batutuwan da suka jibanci tsaron abinci a nahiyar Afirka.

Taron wanda aka bude a Talatar nan a birnin Khartoum, ya samu halartar karamin ministan ma'aikatar noma a kasar ta Sudan Yaqoub Mohamed Al-Tayeb, da jakadan Sin a kasar Li Lianhe, da kuma kwararru daga Sin da kuma wasu na kasashen nahiyar Afirka su 9.

Da yake tsokaci game da wannan batu, Al-Tayeb ya shaidawa mahalarta taron cewa Sudan na da burin amfani da sakamakon taron na wannan karo, wajen goyon bayan bunkasa sha'anin noma a nahiyar Afirka baki daya.

Shi kuwa a nasa bangare Mr. Li Lianhe cewa ya yi musayar dabaru tsakanin Sin da Afirka a fannin aikin gona da tsaron abinci, zai taimaka matuka wajen samar da daidaito da ci gaba a duniya.

Ana dai fatan taron na wannan karo zai baiwa mahalartan sa damar tattaunawa, da nufin habaka harkar noma a Afirka, ya kuma tallafawa hadin gwiwar Sin da nahiyar ta Afirka a wannan fanni.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China