in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Harin da aka kai a wani sansani dake arewacin kasar Mali ya hallaka mutane 10
2015-08-04 09:58:02 cri
Rundunar sojin kasar Mali ta ce wasu 'yan ta'adda sun hallaka sojoji a kalla 10, yayin wani hari kan sansanin dakarunta dake yankin Tombouctou a kasar ta Mali.

Bangaren sojin Mali da ke a yankin ya fayyace cewa, an kai hari ne da sanyin safiyar jiya Litinin, amma har yanzu ba a tabbatar da waye ya kai harin ba.

A cikin 'yan shekarun nan dai ana ci gaba da dauki ba dadi a yankin arewacin kasar ta Mali. A kuma ranar 15 ga watan Mayu sojojin gwamnatin Mali da dakarun dake dauke da makamai da ke yankin arewacin kasar suka daddale yarjejeniyar samar da zaman lafiya, a birnin Bamako, sai dai muhimman rukunonin 'yan adawa 3 na dakarun MNLA na kasar ba su halarci bikin rattaba hannu kan yarjejeniyar ba.

A kuma ranar 20 ga watan Yuni, wakilan kungiyar MNLA sun kai ga sa hannu a yarjejeniya, matakin da ya nuna cewa an daddale yarjejeniyar zaman lafiya a kasar ta Mali, ko da yake hakan bai sanya an dakatar da kaiwa sojojin Malin hare-hare a kai a kai ba. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China