Kafar ta ce hukumar ta shaida cewa rundunar tsaron Rasha ta samu wannan nasara ne a jiya Lahadi. Ta ce wadannan mutanen sun shiga kungiyar IS a kwanan baya, kuma suna aikata laifuka masu alaka da ta'addanci, ciki hadda kashe ma'aikatan gwamnati, da neman kudi daga masana'antu ta barauniyar hanya. Rundunar tsaron kasar ta lura da tafiye-tafiyen su, ta hanyar sa ido kafin su kai ga kai musu hari.
Bisa labarin da kamfanin dillancin labaru na TASS na Rasha ya bayar, an ce, bayan da aka yi kwarya-kwaryar bincike, an gano cewa a cikin 'yan ta'addan da aka kashe, har da wanda ya kulla makircin kai hare-hare ga gwamnatin Groznyy dake kasar ta Rasha a shekarar 2014.
Yanzu haka dai Rasha na fuskantar babban matsin lamba a fannin yaki da ta'addanci. Kaza lika hukumar tsaron kasar ta ce a yanzu haka 'yan ta'adda na yunkurin shiga kasar ta kan iyakokin kasashe da dama. (Bako)