in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An samu rarrabuwar kawuna game da babban zaben kasar Burundi
2015-07-22 10:52:42 cri

An gudanar da babban zabe a kasar Burundi a jiya Talata, inda masu zabe kimanin miliyan 3.8 suka kada kuri'un su, duk kuwa da kauracewa zaben da manyan jami'yyun adawar kasar suka yi.

A cikin 'yan takara 4 dake neman darewa kujerar shugabancin kasar hadda shugaba mai ci Pierre Nkurunziza, wanda kuma shi ne dan takarar jam'iyyar sa ta FDD, yayin da sauran 'yan takara 3 suka fito daga jam'iyyun dake kawance da FDDn, a cewar masu binciken al'amuran siyasa.

Kakakin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasar ya ce, da fari akwai 'yan takara 8 da suka nuna burin su na shiga zaben, kafin dan takarar babbar jam'iyyar adawar kasar wato Agaton Rwasa, da wasu 'yan takarar 3 sun janye daga shiga zaben, sakamakon zargin da suka yi cewa ba za a yi gaskiya da adalci a yayin zaben ba. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China