in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban hukumar zaben Najeriya ya kammala wa'adin aikin sa
2015-06-30 20:48:39 cri
Rahotanni daga Najeriya na cewa shugaban hukumar gudanar da zaben kasar mai zaman kanta Farfesa Attahiru Jega, ya yi ban-kwana da ofishin sa, bayan kammala wa'adin aiki na shekaru 5 a karo na biyu.

A ranar Talatar nan ne dai Farfesa Jega ya kammala wa'adin aikin na sa a hukumar ta INEC tare da wasu kwamishinonin hukumar su 6.

Yayin wani kwarya-kwaryar taro da ya gudana a helkwatar hukumar ta INEC dake birnin tarayyar kasar Abuja, Jega ya mika ragamar shugabancin hukumar ga babban kwamishinan ta Mohammed Wali dan asalin jihar Sokoto, wanda zai zamo mukaddashin shugaban hukumar gabanin nasa sabon shugaba.

Tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ne dai ya damka wa farfesa Jega jagorancin hukumar ta INEC a watan Yunin shekarar 2010, bayan cikar wa'adin tsohon shugaban ta Maurice Iwu.

Ya kuma jagoranci manyan zabukan kasar guda biyu, wato na shekarar 2011, da kuma na wannan shekara ta 2015.

Farfesa Jega ya kasance shugaban hukumar zaben Najeriya na farko a tarihi, wanda ya taba gudanar da manyan zabukan kasar har karo biyu.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China