Tawagar ta ce sassan dakarun kasar sun tafka ta'asa, tare da keta mutuncin bil'Adama. Ya kuma bada misali da yadda dakarun SPLA da na kawayen ta dake gundumar Mayom, suka rika farwa fararen hula a yankin.
An ce dakarun sun rika yiwa mata fyade, tare da wawashe dukiyoyin al'umma. Baya ga kuma kauyuka da dama da suka tarwatsa, lamarin da ya tilasawa kimanin mutane 100,000 tserewa daga gidajensu.