in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Harkokin zuba jarin Sin a Afirka na karkata ga fannin masana'antu inji bankin duniya
2015-06-30 19:39:31 cri
Bankin duniya ya ce lokaci ya yi da kasashen Afirka za su dada inganta shirin su, na samar da kyakkyawan yanayin zuba jari, musamman ma a wannan lokaci da jarin da kasar Sin ke zubawa a nahiyar ke karkata ga fannin bunkasa masana'antu.

Hakan dai na kunshe ne ciki wani rahoto da bankin na duniya ya fitar a Talatar nan. Rahoton ya kara da cewa a baya Sinawa masu zuba jari na maida hankali ne ga fannin ma'adanai da gine-gine, amma a yanzu hakan na sauyawa, inda nahiyar kasar ke kara yawan jarin ta a fannin sarrafa kayayyaki daga masana'antu.

Rahoton ya ce daukar matakan samar da managarcin yanayin zuba jari, zai baiwa Afirka karin damar cin gajiya daga dinbin jarin da take samu.

Babban bankin duniya ya fitar da wannan rahoto ne yayin wani taro kan harkar zuba jari a Afirka , wanda bankin, da kasar Sin da kuma kasar Habasha suka yi hadin gwiwar shiryawa a birnin Addis Ababa.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China