in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya gana da shugabannin tawagogin kasashen duniya da suka halarci bikin rattaba hannu kan yarjejeniyar kafa bankin AIIB
2015-06-29 15:51:22 cri

A yau ne, Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugabannin tawagogin kasashen da suka halarci bikin rattaba hannu kan yarjejeniyar kafa bankin saka jari da samar da muhimman ababen more rayuwa a kasashen Asiya wato AIIB da ya gudana a nan birnin Beijing.

Da farko, a madadin gwamnatin Sin, shugaba Xi ya mika sakon murnar kaddamar da bikin rattaba hannu kan yarjejeniyar. Sannan ya yi nuni da cewa, Sin ta yi tayin kafa bankin AIIB ne, da nufinn ci gaba da inganta habakar muhimman ababen more rayuwa a kasashen Asiya da karfafa hadin gwiwa a tsakaninsu, don cimma burin samun bunkasuwa tare. Wannan yarjejeniya ta samu karbuwa daga kasashen Asiya da sauran kasashen duniya.

Shugaba Xi ya jaddada cewa, yau, mambobin kasashen sun bi turbar akidar hadin gwiwa da bude kofa ga sauran kasashe don daddale yarjejeniyar.

Ya ce, muddin aka ci gaba da bin akidar hadin gwiwar bangarori daban daban,babu makawa za a kafa wani sabon dandalin samun moriyar juna, don kara ba da gudummawa ga kokarin da ake na samar da muhimman ababen more rayuwa a kasashen Asiya.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China