in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira da a gaggauta daddale yarjejeniya game da batun nukiliyar Iran
2015-06-24 11:19:54 cri
Mataimakin zaunannen wakilin Sin dake M.D.D. Wang Min, ya ce ya zama wajibi a daddale yarjejeniya game da batun nukiliyar kasa Iran daga dukkanin fannoni ba tare da wani bata lokaci ba.

Mr. Wang ya kara da cewa, matakin zai yi amfani kwarai a fannin kiyaye tsarin hana yaduwar makaman nukiliya a duniya, baya ga samar da zaman lafiya da zaman karko a yankin Gabas ta tsakiya. Ya ce kasar Sin za ta ci gaba da shiga shawarwarin warware batun nukiliyar ta Iran daga duk fannoni kuma cikin dogon lokaci yadda ya kamata.

A jiya Talata ne aka gudanar da taron kwamitin sulhun M.D.D., inda aka saurari rahoton da kwamitin kakaba takunkumi ga kasar Iran na M.D.D. ya mika. A cikin jawabinsa Wang Min ya ce kasar Sin tana ganin cewa, dukkanin bangarorin da abun ya shafa na da alhakin gudanar da kudurin da kwamitin sulhun M.D.Dr ya tsaida, game da kakaba takunkumi ga Iran cikin tsanaki. Sai dai ya ce takunkumin ba zai zama makasudin M.D.D. ba, domin kuwa kamata ya yi a sanya himma wajen warware batun nukiliyar Iran ta hanyar siyasa. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China