in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Algeriya ta soki harin Boko Haram a jamhuriyar Nijer
2015-06-20 18:29:11 cri
Kasar Algeriya ta yi suka game da harin da mayakan Boko Haram suka kai ma fararen hula a garin Diffa dake Jamhuriyar Niger, a ranar Jumma'an nan ta bayyana jajenta ga iyalan wadanda harin ya rutsa da su tare da tabbatar da goyon bayanta ga al'umma da gwamnati na Niger baki daya.

Kakain ma'aikatar harkokin wajen kasar ta Algeriya Abdelaziz Benali Cherif kamar yadda kamfanin dillancin labarai na APS ta ruwaito, yace wadannan munanan hare hare da 'yan ta'addan suka aiwatar a jajibirin wata mai tsarki na Ramadan ya bayyana irin mummunar aniyarsu.

An labarta cewa mayakan na Boko Haram sun kai hari ne a kauyuka biyu a kudancin Niger a daren Laraba, tare da hallaka mutane fiye da 30 galibin su mata da yara.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China