in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka rasu sakamakon harin kunar bakin wake a Chadi ya kai mutum 37
2015-06-17 19:06:38 cri
Yawan mutanen da suka rasu, sakamakon harin kunar bakin wake da wasu mahara suka kaddamar a kasar Chadi ya kai mutum 37, ciki hadda maharan su 4.

Shugaban kasar Idriss Deby ne ya bayyana hakan, cikin wani jawabi da gidajen talabijin na kasar ta Chadi suka watsa a jiya Talata.

Deby wanda ya yi Allah wadai da tagwayen hare-haren bama-baman, ya bayyana aika-aikar a matsayin tsantsar rashin imani, yana mai cewa ko shakka babu wadanda suka kitsa wannan ta'asa za su hadu da fushin shari'a.

Daga nan sai ya bayyana cewa kasar sa ba za ta karaya ba, ko da kuwa wace irin barazana 'yan ta'adda za su gabatar. Ya kuma yi kira ga al'ummar Chadi da su kwantar da hankulan su, tare da kara hada kai da jami'an tsaro, wajen dakile duk wani mataki daka iya haddasa tashin hankali a kasar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China