in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya halarci taron kolin AU karo na 25
2015-06-16 10:55:03 cri
Manzon musamman na gwamnatin kasar Sin, kuma mataimakin ministan harkokin wajen kasar Zhang Ming ya halarci taron kolin kungiyar AU karo na 25 da taron ministocin hukumar zartaswar kungiyar AU karo na 27 daga ranar 10 zuwa ranar 15 ga wata a birnin Johannesburg dake kasar Afrika ta Kudu.

A ranar 15 ga wata, yayin da Mista Zhang ke ganawa da shugabar hukumar zartaswa kungiyar AU Nkosazana Clarice Dlamini-Zuma, ya mika sakon taya murna da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aikawa taron koli na kungiyar AU a wannan karo, inda ya ce, a halin da ake ciki yanzu, hadin gwiwar da ke tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika na samun babbar dama, akwai makoma mai haske wajen raya shi. Kana, Sin na gaggauta inganta hadin gwiwa da kasashen Afrika, don cimma burin raya hadin gwiwa a fannonin sufuri da kayayyakin more rayuwar jama'a, da tattauna matakan da za a dauka a fannin kiwon lafiya don hana yaduwar cutar Ebola.

A nata bangare, Madam Zuma ta gode wa shugaba Xi da ya mika sakon taya murna ga taron, kuma ta ce, kungiyar AU tana sa ran ci gaba da karfafa hadin gwiwa a fannonin sufuri da kayayyakin more rayuwar jama'a, da kiwon lafiya, da aikin gona, da horar da ma'aikata, da samar da zaman lafiya da karko da sauransu, don cimma burin samun moriyar juna.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China