in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka rasu sakamakon cutar MERS a Koriya ta Kudu ya karu zuwa 16
2015-06-15 14:07:21 cri
Bisa labarin da ma'aikatar kula da kiwon lafiya ta Koriya ta Kudu ta bayar, an ce, a cikin mutanen da suka kamu da cutar nan ta MERS, akwai wani namiji mai shekaru sama da 50, da wani mai shekaru sama da 60 da suka rasu, wanda hakan ya kara yawan mutanen da suka mutu sakamakon cutar ya zuwa mutane 16. Ban da wannan kuma, akwai karin mutane 5 da aka tabbatar sun kamu da cutar a birnin Soeul, inda bisa jimillar yawan mutanen da aka tabbatar sun kamu da cutar ya karu zuwa 150.

Bisa labarin da kamfanin dillancin labaru na Koriya ta Kudu ya bayar, an ce, wani ma'aikacin jinya da ya kamu da cutar kuma ake kula da shi a asibitin Samsung ya yi fama da zazzabi a ranar 2 ga wata, sannan a ranar 10 ga wata, aka fara ware shi.

Wannan ma'aikaci dai ya taba duba lafiyar wasu darurruwan mutane, abin da ke nuna cewa, ya taba mu'amula da wadannan mutane kai tsaye, ko kuma ta wata hanyar. Bisa labarin da aka bayar, an ce, an dauki wannan ma'aikaci ne daga wani asibiti zuwa asibitin Samsung dake Soeul, don haka ba a san irin matakan kandagarki da aka dauka kan ma'aikatan jinyarsa ba, kuma kusan mako guda ke nan ba a killace su ba, don haka ake ganin asibitin ya yi babban kuskure wajen daukar matakan hana yaduwar cutar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China