in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin da hukumar FAO sun kulla sabuwar yarjejeniyar hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa
2015-06-08 13:34:13 cri
A jiya Lahadi ne kasar Sin ta kulla wata sabuwar yarjejeniya tare da hukumar abinci da aikin gona ta MDD FAO, inda kasar ta Sin ta alkawarta samar da dalar Amurka miliyan 50, ga asusun hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashe masu tasowa karkashin hukumar ta FAO.

Ana sa ran amfani da kudaden ne wajen taimakawa kasashe masu tasowa wajen bullo da tsarin aikin gona da samar da abinci mai dorewa.

Hukumar FAO ta bayyana cewa, za a yi amfani da wadannan sabbin kudade da kasar Sin ta samar wajen bunkasa musayar dabaru a tsakanin kwararrun kasar Sin a fannin aikin gona, tare da takwarorin su daga kasashe masu tasowa, musamman ma kasashen dake yankunan tsakiyar Asiya, da tsibiran tekun Pacific, da na nahiyar Afrika, da kuma Latin Amurka wadanda suka fi fama da karancin abinci. (Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China