in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Muhammadu Buhari ya halarci taron G7
2015-06-08 11:02:14 cri
Mai magana da yawun shugaban Najeriya Malam Garba Shehu, ya ce bisa goron gayyata da taron G7 ya gabatar ga shugaba Muhammadu Buhari, yanzu haka shugaban na Najeriya ke halartar taron koli na kungiyar ta G7, wanda shi ne taron kasa da kasa na farko da shugaban Najeriyar ya halarci tun kama aikin sa.

Rahotanni sun ce ministan harkokin wajen Birtaniya Philip Hammond, ya shaidawa Buhari firaministan kasar Birtaniya David Cameroon game da halartar sa taron na G7, yayin bikin rantsuwar kama aikin da aka gudanar a Abuja, a ranar 29 ga watan Mayun da ya shude.

Firaministan kuma na sa ran shagaba Buhari zai halarci taron inda zai gabatar da wasu kudurori game da Najeriya.

Kafin hakan, a 'yan kwanakin baya yayin ganawar sa da firaministan Birtaniya a birnin London, Mr. Cameroon ya alkawarta baiwa Nijeriya taimako, musamman a fannin yaki da masu tsattsauran ra'ayi, da dakile bakin haure na haram daga kasashen Afrika. A sa'i daya kuma, David Cameroon yana sa ran Buhari zai sa hannu kan yarjejeniyar raya dangantakar abokantaka, ta tattalin arziki da ke tsakanin kungiyar EU da Afrika, wadda tuni kasashen Afrika da dama suka amince da ita.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China