in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya jaddada muhimmancin gwaje-gwajen da ake gudanarwa kan kwaskwarima
2015-06-05 20:18:37 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi kira ga jami'ai da kada su yi sanyi a gwiwa wajen aiwatar da gwaje-gwaje a kokarin da ake na zurfafa yin kwaskwarima.

Shugaba Xi yayi wannan kiran ne a yau jumma'a lokacin taro karo na 13 na kungiyar jagoranci na tsakiya akan ayyukan zurfafa kwaskwarima gaba daya, wanda aka kafa a watan Decemer shekara ta 2013 domin tafiyar da ayyukan kwakwarimar kai tsaye.

A lokacin taron shugaba Xi ya jaddada muhimmancin gwaje-gwajen da ake gudanarwa. Ya ce akwai bukatar kara kokarin ganin cewa wadannan gwaje-gwaje an tafiyar da su yadda ya kamata, wanda shi ne mabudin da zai sa sauran kwaskwarimar baki daya ya samu makoma mai kyau.

A wajen taron kungiyar ta amince da tsarin da aka fitar akan kwaskwarimar na kamfanonin mallakar kasa da bangaren shari'a.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China