in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta jaddada aniyar tabbatar da zaman lafiya da karko a tekun kudu ta kasar
2015-06-04 19:34:20 cri
A ranar alhamis din nan kasar Sin ta jaddada aniyar ta ta hada hannu da takwarorin ta na kudu masu gabashin yankin Asiya domin samar da zaman lafiya da karko a tekun kudancin kasar.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin Madam Hua Chunying ta tabbatar da hakan lokacin zantawa da manema labarai tana mai cewa tsarin kasar akan tekun kudancin ta a bayyanne yake kuma akan kari abinda ba za'a canza ba.

Madam Hua tana mai da martani ne dangane da rahotannin mujallar walla street Journal na kasar Amurka da ke cewa yadda kasar Sin ke harkokin raya tsibirin tekun bai hargitsa daidaito ba sai ma ya dawo da hakan. Ta tabbatar da cewar Sin zata cigaba da aiwatar da ayyukan zaman lafiya da daidaito a kan tekun na kudancin ta da sauran kasashen yankin kudu maso gabashin Asiya wato ASEAN, za ta warware matsalolin da ake fuskanta ta hanyar tabbatar da tattaunawa da tuntuban juna, da kuma karfafa ka'idojin da tsarin yankin.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China