in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin kasar Sin a M.D.D. ya yi kira da a kiyaye sakamakon da aka samu wajen yaki da cutar Ebola
2015-06-03 11:40:43 cri
Mataimakin zaunannen wakilin Sin a M.D.D. Wang Min, ya ce kawo yanzu ba a kai ga tabbatar da sakamakon da aka samu game da yaki da cutar Ebola ba, sabo da haka, ya kamata kasashen duniya su yi hattara wajen daukar matakan tabbatar da kawar da cutar.

Mr. Wang ya bayyana hakan ne yayin wani kwarya-kwaryar taron da aka shirya a M.D.D. karo na 68, musamman ma domin dakile cutar Ebola, inda ya ce ya kamata kasashen duniya su karkata hankulansu zuwa ga yaki da cutar, da kuma sake gina yankunan da ta yiwa ta'adi.

Wang Min ya ce, Sin na kokarin tattaunawa da kasashen da abun ya shafa, a wani mataki na tsara shirye-shiryen da suka dace a fannin hadin gwiwa tsakaninsu. Haka kuma Sin ta yi shawarwari da kungiyar AU, don kafa cibiyar yaki da cutar a nahiyar Afirka, tare da gudanar da tarurrukan horaswa 12 a nahiyar, a wannan shekara ta bana.

Wang Min ya kara da cewa, Sin ta ba da kudin karo-karo da yawansa ya kai dalar Amurka miliyan 6, ga asunsun da MDD ta kafa, don taimaki kasashen Afrika wajen yaki da cutar, kuma tana shirin ba da karin kudade a nan gaba. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China