Hankali ya tashi a Lesotho sakamakon labarin tserewar Mr Thabane bayan harin da aka yi kokarin kai mashi, in ji rahoton.
Mr Thanbane yace bukatar shi na son jami'an 'yan sanda su bashi kariya bai samun amincewar gwamnatin kasarsa ba.
Tsohon firaministan dai wanda shi ne shugaban jam'iyar adawa ta ABC sun fadi zaben 'yan majalissar dokoki da aka yi a watan Fabrairu. Ya dai tsere ne lokacin da majalissar dokokin ke mahawara a kan kasafin kudin kasar.(Fatimah Jibril)