in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Sin ya gabatar da ka'idoji 4 wajen inganta hadin gwiwa da kasashen duniya a fannin masana'antu
2015-04-28 16:15:09 cri
A yau Talata 28 ga wata, ministan harkokin wajen Sin Wang Yi ya ce, yayin da kasar Sin take hadin gwiwa da ragowar kasashen waje a bangaren masana'antu da sauran sana'o'i, kasar ta nace ga bin mutumci, da yin hadin gwiwa da samun moriyar juna, da bude kofa ga kasashen waje tare da yin hakuri da masu zuwa, da daukar matakai bisa tsarin kasuwanci.

A yau ne, aka kaddamar da taron tattaunawa karo na 11 a ma'aikatar harkokin wajen Sin,karkashin taken, "Leka lardin Hebei na Sin, don yin hadin gwiwar masana'antu tsakanin kasashen duniya, da samun moriyar juna". A jawabinsa wajen taron, ministan harkokin wajen na Sin ya ce, har kullum kasar a tsaye take don shiga cikin hadin gwiwa tsakanin kasashen duniya a fannin masana'antu da sauran sana'o'i.

Yana mai cewa, dalilin da ya sa, Sin ta inganta hadin gwiwa da kasashen duniya a wannan fanni, shi ne don kokarta canja salon bunkasuwar tattalin arzikinta, da biyan bukatun kasashe masu tasowa. Hakan a cewar ministan, zai taimakawa kokarin kafa sabon nau'in dangantakar kasa da kasa ta hadin gwiwa da moriyar juna.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China