in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ziyarar shugaba Xi a Pakistan da Indonesia ta alamta ra'ayin hadin kai da fatan samun makoma guda
2015-04-25 17:28:02 cri
A ranar Juma'a 24 ga watan nan ne shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya dawo gida, bayan kammala zayarar aiki a kasar Pakistan, da kuma halartar taron shugabannin kasashen Asiya da Afirka, da bikin cika shekaru 60 da gudanar taron Bandung, wanda aka yi a biranen Jakartan kasar Indonesia.

A cewar minsitan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, wannan ziyarar aiki da shugaban na Sin ya gudanar tsakanin ranekun 20 zuwa 24 ga wata, ta alamta burin da Sin ke da shi na tabbatar da hadin kai tsakanin kasashen duniya, da kuma kudurin samun makoma ta bai daya tsakanin ta da makwaftanta, da ma burin cimma nasarar aiwatar da sabon salon dangantakar kasa da kasa.

Ya ce ziyarar ta kuma nuna fatan da ake da shi na karfafa hulda tsakanin kasar Sin da kasashen biyu, da kuma huldar ta da sauran sassan duniya baki daya, musamman ma game da batutuwan da suka jibanci siyasa da tattakalin arziki.

Mr. Wang ya kara da cewa kasar Sin ta bada babbar gudummawa ga nasarar taron Bandung da aka gudanar a karon farko a shekarar 1955, taron da ya maida hankali ga batun karfafa hadin gwiwa tsakanin kasahen Asiya da na Afirka, da kuma sauran kasashen masu tasowa.

Ministan harkokin wajen kasar Sin ya ce babban al'amari ne, ganin yadda bayan shekaru 60, shugabannin Asiya da na Afirka suka sake haduwa a Indonesia, domin gudanar da wannan taro mai matukar muhimmanci, wanda a wannan karo ya maida hankali ga zakulo hanyoyin bunkasa tunanin taron na Bandung, wato batun hadin kai, da abuta, da kuma marawa juna baya.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China