in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Sin ya halarci bikin tunawa da cika shekaru 60 da yin taron Bandung
2015-04-24 15:18:26 cri
Shugabannin kasashen Asiya da Afrika sun halarci wani biki a birnin Bandung dake kasar Indonesiya don tunawa da cika shekaru 60 da shirya taron Bandung, da kuma zagayowar cika shekaru 10 da kulla dangantakar abokantaka ta sabon nau'i bisa manyan tsare-tsare da ke tsakanin kasashen Asiya da Afrika, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci bikin.

Bisa ajandar da aka tsara, a wannan rana da misali karfe 9 da minti 20, shugabannin kasashen Asiya da Afrika sun taka sayyada daga otel din Savoy Homann zuwa ginin Gedung Merdeka wato inda aka shirya taron Bandung a lokacin baya, wannan tafiya tana da ma'anar tarihi, saboda kafin shekaru 60 da suka wuce, tsoffin shugabannin kasashen Asiya da Afrika sun yi wannan tafiya ne, don halartar taron. A ranar yau, shugabannin kasashen Asiya da Afrika, sun yi tafiyar ne domin tuna da tarihi, da kuma yada akidar hadin gwiwa, sada zumunta da sauransu.

Daga bisani kuma, an yi bikin tunawa da taron Bandung a cikin ginin Gedung Merdeka.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China