in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zababben shugaban kasar Nigeriya ya goyi bayan a samar da kariya akan 'yan Nigeriya a Afrika ta kudu
2015-04-19 16:43:13 cri
Zababben shugaban kasar Nigeriya mai jiran gado Muhammadu Buhari ya bayyana goyon bayan shi akan matakin da gwamnatin Nigeriya ta dauka don bada kariya ga 'yan kasar ta dake kasar Afrika ta kudu daga harin nuna kiyayyar baki mazauna da ake kai masu.

A cikin wata sanarwar da kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua ya samu daga sfishinsa a Abuja, tsohon shugaban mulkin soja yanzu kuma zababben shugaba a karkashin jam'iyyar APC, yace ofishin jakadancin Nigeriya ya dauki matakin da ya dace na shawartan duk 'yan Nigeriya da su rufe shagunansu tare da kaurace ma yawo a garin kowa ya zauna a gida.

Muhammadu Buhari yace 'yan Nigeriya a Afrika ta kudu ya kamata su bi doka da oda na wannan kasa mai masaukinsu. Ya kuma yaba ma gwamnatin Nigeriya game da shawarar da ta yanke na sa ido kwarai akan duk wani cigaba dake wakana a kasar ta Afrika ta kudu tare da kwaso 'yan kasar ta zuwa gida da zaran an ga al'amurra zasu kazanta. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China